Friday, 16 September 2016

KISHIYOYINA 51TO 69

. Home Home About Me About Me Navigation Navigation

BARKA DA ZUWA DANDALIN HAUSA NOVELS CALL /BARKA DA ZUWA DANDALIN HAUSA NOVELS CALL /WHATSAPP ME @ WHATSAPP ME @

Search

KISHIYOYINA

Posted by Mymounerh basheer on 07:25 PM, 31-Aug-16

Under: KISHIYOYINA

Assalamu'alaikum___!!

, [12:08pm, 31/08/2016] Queen meemiluv: , ,

KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

53

WASHEGARI!

Kamar wajen k'arfe goma duk su Mariya sun hallara.

Malam ya na cikin d'akin sa duk suka je su ka zazzau na suka

gaishe shi amma ko d'aga ido bai ba balle ya kalle su,sai da

ya gama abun da yake ya juyo yace" wato abunda kukai kun kyau

ta kenan?

Shine don ku kashe wa yarinya aure zaku je kuyi fad'a da

muta ne ko ?to meya kaiku? cikin in ina mariya tace"... Baba

wlh bugon waya k'awarta tai tana kuka wai sun kashe ta shine

hankali na ya tashi muka je duba ta shine matan sa suka kama

mu da fad'a "

Duk da haka kun deyi kus kure kun ke ta haddi tun da a gidan

su kuka je ,"to kar naji kar na gani duk abunda zai samu

zahra kar waccen ta kuma d'ibar Jiki taje can na gaya muku "

kuna ji na? "Suka ce eh" ha kan yai ta musu Nasiha san nan ya

sallame, su d'akin Goggo suka shiga suna ta maida magana

,Aminu dake zaune ya na break fast ya had'e rai shi kam yana

tausayin yayar sa ,wan nan ke nan.

,Queen meemi

KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

54

Malam kam samun Alhaji yai da zen cen san ja gida .Alhaji ya

ce "ay ba matsala nima abun yasoma ban tsoro sam matan nan

basa tsoron Allah," ,ya ce "akwai wani gida a Hotoro G.R.A

sabo ne k'arami na gina shi da 'yan haya zansa amma yanzu sai

ta koma can ,gaisa wa suka kuma yi cikin jin dad'i da fahim

tar juna.

Zahra kam cikin kwanciyar hankali ta koma G .R.A wan da su

Anty Mariya suka taya ta tsara gidan hankalin ta akwance

,yanda Matan sa keda mota da driver dake kai su unguwa ha kan

yasa ya samu k'aramar mota tare da driver wan da zai dun ga

kai ta unguwa ,tare da mai aikin ta Lantana.

Sai bayan komawar zahra .G.R.A da kwana 2 san. Malam ya

takura wa alhaji ya dawo da su Uwani. Amma ya ce" ban da su

tsigai da Nadiya don ya gaji da rik'e 'ya'yan da basu da

mutunci ,ha kan de Malam ya tattaushe shi ("kaji suru kan

arxiki" da k'yar ya hak'ura za'ada wo har da su Amira

d'in.

Urs Queen meemi

NG WRITERS ASSOCIATION [12:13pm, 31/08/2016] Queen meemiluv: ,Queen meemi

KISHIYOYINA

55

Kwanci ta shi ba wuya a wurin ALLAH Zahra ta doshi wata

d'aya a sabon Gidan ta inda zaman lafiya ya dad'a wan zuwa

tsakanin ta da Alhaji,tarai taraya kam ta na shan ta gun

Alhaji ayanzu zuciyart a ta d'an samu nutsuwa,ga mai aikinta

Lantana mai kirki suna zaman ,lafiya ta je gidan Maman ta har

sau 2, ita kan ta taji da d'in ga nin yanda hankalin Zahra ya

kwan ta ,domin da duk abinda ta ke ciki ,Aminu na ga ya ma ta

,Adduar Uwa kar b'ab'b'iya ce kullum dare ba ta bacci. Tana

wa 'yar ta Adduar samun salaama a auren ta wan nan

kenan.

Suna zaune ....A falo suna kallon tashar zee alwan .Lantana

daga gefe suna d'an hira,ji tai ana buga kofa da k'arfi da

sauri Lantana taje ta bud'e ....,Mutanen ne su ka fa ra shigo

wa. Arazane Zahra ta ta shi !.,

Amma se ta basar ta na ce wa" ai baki mukai ",kalle-kallen

falon suke, suna jin jina kai ,cike da gadara ko wacce ta ja

kujera,ta Zauna. Uwani ta na lalle Alhaji hmmm+mmm! Lemo

Lantana ta kawo mu su zahra kam gaishe su ta hau yi .Magajiya

ta ce" ke ba gaisuwa mu,kazo yi ba san nan ba Lemo mu kazo

sha ba don kin san akwai agida,wallhi kar kiga kin dawo nan

ba k'yaleki mukai ba ",hajiya Zainab ta ce "Jibi gida wai ita

ka d'ai lalle. Alhaji abayya ne ma sai ya nu na rashin adalci

.

Zahra kam ta ta sun kwi da kai tana jan yo adduar (ALLAH

HUMMA AJIRNI FI MUSIBATI WA AKLIFNI KAIRAN MINHA)seyi ta ke

Azuciyar ta tare da karan ta (LAHAULA WALA KUWATA ILLA

BILLAH)domin kauce wa sharrin su don tsoron su kam ta keji ha

kan su ka gama magan- ganun su da bud'e- bud'en su suka

tafi,sun so zahra ta tan ka ,ita kam tai karatun ta

nutsu,bayan futar su taja ajiyar zucia da suka fita

lafiya ,11:29Queen meemi

KISHIYOYINA NA Mymouner Basheer

56

suna zau ne afalo Jummai k'awar Magajiya ta zo ,tana

tambayar su Zahra su ka ga ya ma ta ai ta bar gidan ,nan ta

sa shewa amma nai muku murna,"Jummai kenan gida fa yajan ja

ma ta" ,da fe kirji tai kai haba de? Ta ce" wallahi amma

wallhi kun yi sa ke ai wan nan gwan da ace ta na gidan nan

yan zu ku ka san irin dukiyar daze na sakar mata kuwa lalle

na raina kishin ku,(hmm sunki yadda da kaddara,RUBUTECCEN

AL'AMARI NE LITTAFIN MY TWINNY BESTY BILLY,tun fil azal,amma

su kishin su yaki bari su gane.

Uwani ta ce" wallahi kai na duk ya kunce dabara ta k'are,mun

yi na bokan abanza,jummai ta ce' se ku had"a da makirci ai

,mata fa kuke kuma manya ,yo wane dare ne Jemage bai gani

ba,?Magajiya ta ce" sai daren mutuwar sa",ta shi tai ta kama

kun nen Magajiya ta rad'a ma ta, nan suka k'yalk'yale da

dariya kai Jummai shiisa nake son zama da ke akwai wayo,ni

d'in ai ba wasa ba ce" nan ta fesa wa su Uwani duk suka sa

dariya ,ina daga gefe ara kub'e don son jin meta fad'a amma

tsoron kar su zaune ni shiisa na koma gefehmm mamaki ne taf

afuska na ta yan da. Alhaji ya had'a matan nan basu san komi

ba sai ci da sha,da Jiran dukiya sa .Allah kasa mufi k'arfin

zuciyar mu.

Yau daya ke Alhaji ya je gidan matan sa, shiga yai cikin

fara' a su ka tarbe shi sai hidima suke mai shi kam mamaki

duk ya ishe shi hira aka zauna ana yi,Magajiya ya ce tasa

kuka .Alhaji? ya ce "ehem me ke faruwa ne? Nan suka hau bashi

hakuri akan abun da duk sukai wa zahra acewar su sun yar da

da k'addara, ga nin hawaye a fuskar su ya yar da yanu na

bakomi,nan kowacce ta tsiri fadar matsalar ta ta kud'i ,take

duk ya biya musu ,da zai tafi har da cewa agai da

zahra.

Yau zahra ta ta shi da amai kace- kace da Jiri ga ta shin

zuciya ,bayan dawo war. Alhaji ya sa suka ta fi Asibiti

gwajin farko suka ce ta na da ciki 2 month murna kam kamar ya

suma ,ha kan su ka dawo gida.Lantana ke kula da ita hankalin

su kwan ce.Alhaji kam ba wanda ya gayawa don ya tsora ta da

su hajiya duk da sun tuban.

Urs Queen meemi

NG WRITERS ASSOCIATION ®NGA [12:31pm, 31/08/2016] Queen meemiluv: , KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

57

Alhaji ke shi rin fita, da ya ke yau ya na gun manyan matan

,har ya shiga mota da sauri Uwani ta je har da dan russu

nawa,"Alhaji da ma ina nai man alfarma wallahi ka ga Larai ta

tafi ganin gida ,to da ma ko za ka ce Lantana ta zo?" ,saboda

lokacin da ta ke gidan nan da ta re na ke aiken su",ya

ce"

ina ne ?ta ce "kasuwa ne su su ke suyon mai kyau",ya ce" to

inna je zata zo" godiya ta hau hi

Lantana na zuwa suka ja ta d'aki tai mamaki nan ta zauna su

na zaune su uku, Hajiya Zainab ta ce ",kin san aikin da muke

so ki mana"?ta ce "Aa Hajiya, kud'i Uwani ta futo da

shi,kinga wan nan dubu goma ne ,kuma naki," zaro Ido Lantana

tai ,Hajiya duk ni kad'ai suka ce" k'warai ,Hajiya "ku fad'i

kome ne ne zan muku Inde befi k'arfi na ba,"so mu ke duk wani

abu da ke guda na agidan Zahra kina kawo ma na ko me ki ka Ji

kizo ki ga ya mana",ta ce" ai me sauk'i ne Hajia",Hajiya

Zainab ta ce "in de ai kin ki yai kyau za mu k'ara miki dubu

ashirin" dad'i ne ya ka ma ta, da sauri ta ce" ai yanzu ma

Akwai,abun da zan ga ya muku .

Zahra na d'au ke da ciki na wa ta biyu kamar had'in baki ko

wacce ta mik'e tare da zaro ido,ni kam na ce" kuna ta ku

ALLAH Na na shi ,ta ALLAH ita ce gaskiya) tab di Jam in ji

Hajiya Zainab,nan su ka sallame ta, ta ta shi ta tafi dama ta

na da tsohuwar nokia mai tochlight ha kan yasa su ka karb'i

number inta.

Bayan kwana 2 su ka kirawo Lantana Lokacin su na gyaran

d'aki ita da Zahra ,wanka Zahra ta shiga yi,nan su ka Umarce

ta da ta d'au ko mu su Book kowa ne iri ne, inde Hand writing

In Zahra, Lantana ta ce" Hajiya me ne"? Hand writing,tsaki

Hajiya ta sa da ta tu na Lantana ce ashe,nan ta ce" Littafi

mai rubutu Inde kingan shi Kika tabba tar na Zahra ne ki kawo

ma na" ,ta ce" ba Matsala Hajiya ai mai sauk'i ne,"da sauri

ta kashe jin alamar bud'e k'ofa.

,,,,,,,,Queen meem

KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

58

Da ma ce ta samu Lantana Inda ta kalli Zahra ",Anty ga ma

Jakun kunan ki na Makaranta ina zan saka su"? ,nan ta ce" ki

kai mun cikin drower,bayan futar Zahra da sauri ta bud'e

cikin sa' a ta d'auko wani 40leaves ta soka acikin Zanin ta,

sauri tai ta ga ma aikace -aikacen ta ,ta gyara d'akin ta

futa ,wajen la 'asar ta nai mi Izini wai Zata gun Maman ta

daya ke Maman ta ta, ma na aiki a wani gidan masu Hannu da

shuni,ha kan kuwa akai futar ta ba ta zar ce ko ina ba sai

Yakasai,su Hajiya na Zaune agefe ga wata mai sai da Kaya irin

na mata sun barbaje sai siya suke ,ga nin lantana ya sa

Magajiya ta ja ta d'aki ,nan ta zaro Book In ta bud'e

Murmushi tai,

Kallon ta tai ,tace"mene Labari? Lantana ta ce" Jiya ina

d'aki wajen k'arfe. 8 Anty da Alhaji na falo naji ya na

tambayar ta watan cikin na wa tace" mai Uku,(lallema har wani

watan ciki ake tambaya hmm muje xuwa) Sallamar ta tai tawu ce

gidan,inda dad'i ya kashe ta don yau ma sun bata dubu

biyar,Ita aganin ta aiki ya bud'e ma ta,Hmm Lantana A juri

zuwa rafi dai..wata ran tulun zai fashe.

Bayan futar ta suka taru don tsara yan da za su had'a m ata

Makircin (Allah sarki Baiwar Allah ba ma tasan kunayi

ba)kiran Nadiya su kai akan ta samo musu wani k'wak k'wa ran

wanda ya iya Rubutu ,cikin Murmushi Nadiya ta ce" ai kam ina

da shi ",don yan zu Nadiya ba ta Zaman gidan kullum ta na

biye -biye ga Shige wa Maza ,ta dad'e da fara School wa to

Federal College of Education amma in taje ban da bun Maza ba

ta Karatun komi,Carry Ovar ne fall akan ta,kuma Duk Alhaji ne

yai wahalar School in ,wan nan ya sa ta d'au ki Book in domin

ta kaiwa wani Saurayin ta Class Mate na ta ,duk suka ga ya ma

ta abun da za a Rubuta ya zamto iri d'aya da na Zahra ,wan

nan Kenan.

Urs Queen meemi

®NGA , [12:45pm, 31/08/2016] Queen meemiluv: KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

59

Kwanci tashi ba wuya agurin ALLAH cikin zahra ya cika wata

na takwas ,inda take samun kulawa daga gun Alhaji da kuma

gida,

Ab'angaren Manyan Mata kuwa kullum cikin kawo musu gulma ake

amma abi yaci tu ra,daga suje gun wan nan boka se suje can

,duk sun tashi hankulan su akan cikin Zahra,wanda Allah ke

dad'a ikon sa Akan Al amura.

Alhaji ne gaban doctor shi da Zahra ana yin text na ganin

abinda ke cikin ta ,d'ago wa Doctor yai suka gaisa da Alhaji

,yace mai" Congratulation Matar ka na d'auke da twince dau

Maza,da sauri Alhaji ya mike masha Allah ,godiya yai wa

Allah,daya cika mai burin sa ya kalli Zahra da ta sunkwi da

Kai saboda kunya ,yace" Lalle Zahra kin kasance mun SANYIN

IDANIYATA,tauraruwa acikin taurari,shi kam Doctor mamaki ne

k'arara afuskar sa ,yanda kamar Zahra itace matar ,sa shi kam

afarko ma ya d'auka 'yar sa ce ,nan ya basar da tuna

nin.

Tunda suka koma gida Alhaji ke nan nan da Zahra kamar k'wai

Lanatana da ke aikace aikace ,duk gulma na cinta amma babu

dama time da suka shige d'aki har lab'ewa tai,amma taji

shiru,

,Queen meem

kISHIYOYINA QUEEN MEEMI

60

ALhaji ke zaune sai har ha'da Takardu ya ke ya na cikewa

,Zahra ce ta shigo ta Zauna ,tana gaida shi,ta ce" Alhaji ya

kamata na koma gida ko tunda kaga lokacin Haihuwar

yazo,"d'agowa yai ya kalle ta ,Aaa ki Zamanki in kin haihu

sai ki tafi ,shiru tai bata ce komi ba.

D'agowa yai kalle ta ya ce" karb'i wan nan ki gani"?

Karb'a tai ta na dubawa ko ina sai taga ansa hassan and

hussain ,d'agowa tai ta na neman k'arin bayani nan ya ce"

mata duk rabin dukiya ta da kadarori na duk na saka sunan

babies enki,kasa magana tai in banda kallo data ke binshi da

shi,Hawaye ne suka zubo mata ,ta kasa magana abunda ba ta

tab'a yi ba Rungume Alhaji tai ta na godiya ,bayan ta share

Hawayen ta tace" Alhaji ka aje a wajen ka" yace ba

matsala,akasalan ce ta tashi ta fita dakyar.

Zahra na zaune da cikinta duk ya mata nauyi tana shan romon

Kifi ,A lokacin tana watan haihuwar ta ,Lantana bata

nan,gashi tana so ta gyara mata d'a ki,sai wajen 2 Lantana ta

dawo,adede Lokacin Alhaji shima na faka Motar sa,share-

shareLantana ta fara yi,nan ta shiga d'akin Zahra ta gama ta

fito,Alhaji ne Ya kalli Zahra muje D'akiin ki mi Magana nan

suka Shiga ,toilet ta Zarce shikam Alhaji ya kwanta akan

gadon Hannun sa ne yaji yana tabo Kamar Takar da ,d'auka yayi

ya bud'e Wasik'a ce ya gani,da kamar bazai katanta ba sai

kuma yaga kamar irin hand writing in Zahra ,karanta wa ya

farayi cikin tashin hankali,ba inda ya fi bashi mamaki sai

gun da akace" KI KULAMUN DA CIKIN DAKE JIKIN KI DON INA SONSA

MATUK'A

Daga tsohon Masoyinki.

Tashin hankali wanda ba asa masa rana,kansa ne ya fara

juyawa,fitowar Zahra da sauri ya b'oye Takar dar mamakin ta

yake gani tai ya canja ,tace " mai Alhaji meya faru"? Nan

yace" mata kansa ke ciwo tashi yai ya futa,Mamaki k'arara

afuskarta sai ta basar Don ta tuno da kashedin likita kan ta

dena yawan tunani.

Urs Queen meemi

, [12:52pm, 31/08/2016] Queen meemiluv: , ,8:28,

KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

65

Tun da Alhaji ya koma gida ya rasa sukuni ,kamar k'aramun

yaro haka yake kuka,bak'in ciki yai mai yawa ,shi kam ya

shiga rud'ani akan cikin ta don gani ya ke kamar ba na

saba,k'irjin sa ne ya fara ciwo dafe wa yai ,dakyar ya d'auko

Maganin sa ya sha,yad'an samu relief,muk'ulli ya d'auka ya

fito, kiran Lantana yai ya ce" ta shirya ta tafi ,can gidan

ta ciga ba da musu aiki",sunkwi da kai tai" Alhaji ina Antty

ne? ko haihuwar ce?" yace"mata Eh tatfi gida.

Bayan ta had'a kayan ta ta tafi yakasai,bayan taje duk ta

sanar da su Hajiya dad'i ne ya kashe su sai Annashu wa suke

don samun nasara,Hajiya Magajiya ta ce" saura cikin idan ta

haifeshi ma san yanda za ai ",ta fawa sukai na jin dad

'i

Lokacin da Alhaji ya shigo suna lura da shi sam ba shida

walwala,sai tambayar sa suke haka dai suka gama kisisi nar su

,da sun keb'e su hau dariya ,kwana 2 Alhaji ya rasa sukuni ko

abinci baya ci duk ya fad'a,(Allah sarki)su kam sai wadak'ar

su suke don burun su ya cika,sun fudda Zahra aganinsu,to

fah

Tun asuba Zahra ke jin ciwo ,amma bata ga yawa kowa ba har

Saafiya, Goggo na kula da ita sai ta share,don ta kula kwana

biyu tunda ta dawo bata da sukuni ta sha ganin ta tana kuka

.

,Queen meemi

KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

66

Tana cikin d'iban ruwa abuta cikin ta ya murd'a dafewa tai

kuka ta fara,Da sauri Goggo ta taso tace"Zahra kode haihuwar

ce"dama ina kula dake,kiran Aminu tai daya shigo tace"ya samo

mota" cikin yan lokuta ya samo suka tafi Asibitin da take

Awo,Aminu kam waya ya bugawa Malam domin Doctor ya ce" ba

zata iya haihuwa da kanta ba dole aiki za amata,Zuwan Malam

yasa aka nemi wayar,Alhaji amma batta shiga,Ak'arshe dai shi

ya cike Aka shiga da ita d'akin thearter ,Auta sai kuka take

hakan Aminu duk sunyi jugum-jugum saida Malam yai musu magana

suka daina.

Wajen kamar Awowi Aka fito da babies da sauri Goggo ta

karb'a tana "Ikon Allah dama 'yan biyu ne? ,gashi duk maza"

su Auta nan suka fara dariya,norse ce ta fito ta karb'esu

,Malam ya ce" ina Maman su tace" ta na d'akin hutu,kafin kace

mai duk su mariya duk sun hallara har da matan su Atiku duk

yayun ta dai kowa kagani na murna.

Ab'an garen Alhaji kuwa rashin lafiya ya kwantar shi tun

lokacin da ya dawo daga shigowar sa babban falo yaga ba kowa

d'an hayaniya yaji ak'aramin Falo kamar ance ya tsaya yaji

Hajiya Uwani na magana" ai Salele ya iya aiki,shegiya Lantana

akwai iya makirci" ,gaban sa ne ya fadi,yaji suna Zen cen

takarda duk wani abu duk yaji su,har yaji sanda suka bawa

Lantana kud'i ta bawa Salele duk ya gama jin komi dafe kirjin

sa yai,zama yai akan kujera nan yaji mugun tausayin Zahra ta

shi yai zaije d'aki ko gaban sa baya gani sai kawai ya yanke

jiki ya fadi.

Fitowa Bayan sun gama shewar su ganin sa da sukai ak'asa

yasa suka fasa ihun munafunci Hameed nai ya taimaka aka

kaishi Asibiti...................

Urs Queen meemi [1:02pm, 31/08/2016] Queen meemiluv: , KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

61

Tashi tai ta shiga d'akin sa ganin sa tai ya sun kuyar da

kai ,zama tai kan kujera,tace"Alhaji wai meya faru? ,d'gowa

yai taga jijiyoyin kan sa sunyi bur d'un -burd'un da sauri ta

tashi ta komaa kusa da shi tace "Alhaji wai meke faruwa

ne"?

Yace" Zahra kin ban mamaki yanzu duk irin zaman da muke da

ke na d'auki soyayya ta na baki amma ashe amana ta kike

ci,"cikiin tashin Hankali tace" Alhaji ni"! Take hawaye kamar

me sukai ta zubo ma ta,nan ta tsugunna ,tace" Alhaji wallahi

ni ban san. Komi ba" ",D'agowa yai Ai dama bakya sona shi isa

zaki mun hakan ".Tace"wallahi nasan dokokin Allah da k'imar

aure bazan ci amanar ka ba".

Zaro wasik'ar yayi ya mik'a mata "karanta ki gani",bud'ewa

tai hannun ta na rawa ,lokacin da ta gama karantawa k'ara ta

saki tare da dafe ciki ,kuka takeyi cin k'arfin ta Sai kiran

Sunan ALLah mai girma take,da kyar ta tashi ta d'auko Alkir

ani zata dafa,cikin k'rfin Hali ya k'wace ,cewa tai "ka barni

na dafa Alkur ani wallahi tallahi ban san da wasik'ar nan

ba",jikin sa ne yayi sanyi,kamo ta yayi ya rungume ta ,tare

da bata hak'uri tana kuka tana yiwa Wanda yai mata Allah ya

isa,zazzabi ne ya rufeta .

,Queen meemi

KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

62

Lantana ce ga ban Hajiyoyi ,ta ke sanar dasu ,tabbas ta aje

wasikar nan kuma ad'akin ,har ta ke sanar da su ai ,time da

su ka shiga d'akin ta ga lokacin da Alhaji ya fito ransa

Ab'ace,nan suka sa dariya da Alama aikin mu wan nan karan zai

ci,sai b'arar gyad'a suke suma afawa abaki,duniya tai musu

dad'i Nadiya ce ta shigo falon sai taunar chew gum take ,nan

Uwani tace" Nadiya kinsan kuwa su Amira na gab da aure idan

baki fudda miji ba".

Tab'e baki tai zanyi mana" ,ita Amirar wa zata aura"?Hajia

Zainab tace" 'yar gida za ai ita da Hameed ashe sun dad'e

suna soyayya" tashi tai tace" jaraba gaskiya Amira na shigar

mun hanci da kudun dune ,saurayin nawa zata aura ",Amira dake

shigowa falon tace "A ina ya zama saurayin ki? ja jiki Kawai

kije ki nemo naki,Hameed nawa ne" wallahi baki isaba ba cewar

Nadiya"tsigai da ke taje kai tace"kai Anty Nadiya saurayin fa

Amira ne waye bai san suna Soyayya ba duk gidan nan" "Dallah

rufen baki ke wama zaice yana sonki "jibar ki fa,ko tudun

kirki Baki da shi"nan Magajiya tasa baki "Aa Nadiya karfa ki

zak'e duk anfiki Gaskiya,kuma tsigai da kike kushewa Da me

sonta ,kede zauna kina yawon barbad'a,"Nan Uwani tace" ya isa

hakan aiba wani abun take ba".

Tsigai ta tashi zata shiga d'aki ,ta kalli Nadiya tace"ke

kam Anty abu yai miki yawa ,ya kamata kije ki tambayo Ya

Hameed in kin ga sai ya,tabbatar miki da gaskya,"da sauri ta

shige d'aki,Nadiya tace"Wallahi dakin tsaya da saina karai-

rayaki,mai kama da sauro nikam da nake zaune na ce"ita

ku,wai ance da makaho ga ido yace" ni wanka na nake"kun fi

kusa. [1:14pm, 31/08/2016] Queen meemiluv: KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

63

Yau Zahra ta tashi duk bata Jin dad'i daure wa kawai ta ke

yi Lantana na kula da ita ,zuwa tai tace"Anty na ga kamar

bakya jin dad'i ko zaki je ki kwanta kafin Ai sallar la asar

",tace "wallhi kam bari naje na kwanta ko na d'anji

dama-dama" shigar ta d'aki ke da wiya ta d'auko wayar ta ta

bugawa su Hajiya Uwani,sai jin -jina kai ta ke Alamar tana

gane karatun da suke gaya mata,sallama sukai ta kashe.

Da sauri ta d'au mayafin ta, futa can waje tai tana wai -ge

wai ge,waya ta d'auko tana kiran Salele ,"ka ta wo kuwa"?"

tun yaushe gani abayan Layin nan "ta ce" to Lokaci yayi sai

ka zagayo" da sauri ta koma ciki,tana tsaye har ya k'araso

duddu bawa tai ta ga Maigadi na sharar bacci da sauri su ka

shige gidan,adede bayan ko far d'akin zahra Salele ya lab'e

,ko mawa tai ta cigaba da aikin ta ta nayi tana wak'e-wak'e

,k'arar hon d'in mota taji ta wani da ka tsalle,Alhaji nai ya

bud'e falon da sauri ta sun kuya tana gaida shi,tambayar ta

yake ina zahra,nan tace"tana bacci ad'akin ta ,d'akin ya dosa

salele na bayan k'ofa yaji Alamar tafiya ,da sauri yafito

yana k'okarin sa riga ,sai Alamar gudu yake ,wuce Alhaji yai

da sauri,ta ke Alhaji ya bishi ,Lantana ce ta tashi da sauri

Alamar mamaki ta toshe baki,Alhaji bai samu damar kama shi ba

ya gudu.

KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

64

Cikin huci da k'unar rai ya dawo ,Kallon Lantana yai ,wanda

duk ta wani rikice,(Mara gaskiya ko A Ruwa gumi yake) sai kar

-karwa Jikin ta ya ke Alamar muna finci,yace" yaushe wan nan

ya shigo ,d'ago wa tai Alhaji ni ban sani ba wallahi don ina

d'aki ina guga,tsaki yai d'akin zahra ,da sauri Lantana ta

d'au waya ta na gaya musu, Alamar aiki yai kyau,Alhaji ne ya

tsaya bakin k'ofar d'akin yakasa shiga ,hawaye ne ke zuba

,babban Mutum dashi ,Allah sarki baiwar Allah sai sharar

bacci ta ke bata san meke wakana ba,tashin ta yai mutsits

-tsike ido take ,ta kalle shi, " Alhaji yaushe ka dawo"?

hawayen da ta gani Afuskar sa shiya gigita ta, "Alhaji meya

faru "?da katar da ita yai , yace"kinci Amana ta Zahra ran

nan na ga wasik'a kince baki san zance ba yau kuma har gardi

ad'a kinki"WA IYA ZUBILLAHI".

"Amma Zahra Albasa ba tai halin ruwa ba,kin bani

mamaki",kuka take shab'e shab'e ta rasa ba kin magana ,ce

mata yai ta sa hijab din ta,ba musu ta sa suka fita,ta na

kuka. Lantana dake lab'e tasa dariya ("Lalle kud'i ba yanda

basa maida mutum Lantana kenan" hakan yaja ta bai zame ko

inaba sai gidan su, Dede sun tsaya a k'ofar gidan Lokacin

Malam ya dawo daga masallaci,sun gaisa yake sanar mai ai

yakawo Zahra ne Malam yai mamaki don sunyi magana da Alhajin

sai ta haihu zata dawo, Mamaki ya isheshi ,sai bece komi ba

akwatin ta, taja ta shiga cikin gidan k'irjin ta na dukan

uku- uku,shikam akofar gida sukai Sallama ya tafi.

Malam ke tambayar ta Allah yasa ba ta kurawa tai ba ,sai ta

dawo ,hawaye ne ke san zubo mata tace "Aa shine yai ra ayi,"

shide bai gamsu ba amma yak'yale tunda basu ce mai komi

ba,tunda ta shiga d'akin Goggo take kuka ,da taga alamar za

ashigo sai ta rufe Ido Allah sarki baiwar Alllah,"INNALLAHA

MA'ASSABIREEN".

UrsQueen meemi [1:41pm, 31/08/2016] Queen meemiluv: KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

69

Hakan Alhaji na.kwance a sibitin ya saki kudi ana ta hidima

komi waja-waja agidan su zahra Albarkacin twince,Alhaji Tahir

sai kaikawo yake, ranar suna aka yanka raguna manya

manyan,raguna biyu da tirkeken SA kuda daya kaya kam kamar sa

magana,sbd Alhaji akwai alheri zahra ma kam kullm cikin

sabbin kaya take saidai ba ai suna ba saboda rashin lfyar

Alhaji.

Duk wan nan abun da ake hajiyoyin naku basu san maike faruwa

ba,don Alhaji yace kar wanda yagaya musu ko Hameed shuru yai

da bakinsa,yanxu harka ta bude musu kullum cikin karbo

wan.nan karbi wancen Alhaji Tahir kam ko bi ta kansu baya

yi,duk Alhaji yasa Alhaji tahir ya debo mai document nasa nan

ya ware takardun dayasa sunan twince,sukam inbanda suxo su

cika asibiti kamar gidan biki,har an gane su suyi ta ciye

-ciyensu,su nadiya adamo dinki azo ayta karai raya gaban

norses maza da Doctors,

Suna zaune hajiya tace kama ta yai mu fara karbar kudi musan

me muka kama tunda kunga in Alhaji ya mutu bamuda rabo mai

tsoka,kunga Hankalinmu yanzu akwance yake tunda ,'yar nacin

yakoreta ,kuma boka yatabbatr mun cikin jikinta ya zube ,nan

suka tafa to dama zamuyi hasara biyu,duk sun sakace kudaden

Alhaji nagidan suka koma kantunan sa suna karbar kaya da kudi

hankalinsu kwance sam basu damu da rashin lfyar,sa ba saidai

kawai su cika asibitin don kar ace basu zuwa.

KISHIYOYINANA Mymounerh Basheer

70

Kwanci tashi ba wuya agurin Allah ,ZAHRA tayi arba'en sunyi

kyau sosai itada twince ,babies in kamar kadauka ka gudu

saboda kyau,don Zahra nada kyau sosai,duk sai sukai kyanta

sai skin en hussain da tai irin na Alhaji da hancinsa,suna

samun kulawa ta bangaren Alhaji tahir Saboda Alhaji yabude

bakin Aljihu kawai hidima ake musu.kuma kullum sai ankai su

yagansu tunkan tai arbain

Yau kamar kullum sun shirya don yau tacika arbarn en ,nan

Malam yay mata umarni datajegun mijinta ,hakan kuwa akai

tafiya sukai itada auta,Alhaji yaji dadin ganinsu ,tunda

zahra taje take kuka sbd yanda Alhaji duk ya rame ya dada

manyanta, sai dai yanzu yana iya tashi hakan yasa yadau

twince ,nna da nan Zahra tahau hidima dashi,sai wajen

magariba suka tafi,wanda duk wanan abun da akai acikin matan

bawacce tashigo ,dama kullum sai aukin xuwa amma ko ruwa basa

bashi ,sai dai 'ya'yan Alhajitahir maza suke kula dashi kuma

su kwana agun shi wan nan ke nan

Cikin ikon Allah Alhaji ya warware har an sallameshi, yakoma

gida,kowacce saita tsiri nan nan dashi,shikam yanxu yasha

jinin jikinsa da su,sam baya son ganinsu amma bayanda ya

iya,kwana 2 da komawarsa zahra ta koma gidan ta,tare da Auta

daza ta taya ta aiki da mai aiki d'aya,

Hajia uwani ce zaune bayan mota suna hira da driver zai

kaita umguwa nan yake mata barkar haihuwar zahra dafe kirji

tai habade wace zahran yace amaryar Alhaji yace ,haihuwamai

albarka twince ,jitai ta kware sabd kidima ,bashiri tace

yamaida ta gida,tundaga falo ta shiga kiran ,suna fitowa ta

gaya musu ,ai bamu ga ta zama ba hakan yasa suka xari mayafai

,don yanzu basama tambayr alhaji inzaasu fita,gidan

boka

Suna zuwa sun tarar va kowa duksu ukun suka shiga take suka

sanar mai nan yace" mai za ai "?suka had'a baki "akashe

boka"?dariya ya busa wan nan mai sauki ne take ,yabasu wani

laya yace su bunne ,kuma su tabbatar daya daga ciki tafuta

agobe ,taje gidan ita yarinyar ta tsaya awaje zansa d'an

kutunba ya fito da Jaririn ,

To fa masu karatu gareku,me zaku ce da wadan nan azzaluman

mata?

Urs Queen meemi , [5:17pm, 31/08/2016] Queen meemiluv: , Queen meemi

KISHIYOYINA NA

68

Ab'an garen su zahra kuwa ,ta farfad'o amma in banda kuka ba

abunda take sun lallashin amma tak'i shiru sai da Maman ta da

ta zo tai Mata Magana ta bari ,duk da ta san akwai abunda ke

damun ta,Malam ya ga shiru ba Alhaji,gashi wayar sa switch

off ,k'awai sai ya yanke shawarar zuwa gidan.

Bayan fitar sa ya tafi gidan Alhaji ,Maigadi ya tarar ya ke

tambayar sa ko Alhaji na nan? ,take yasanar mai ai Alhaji ba

lafiya ya na Asibiti,sallallami ya fara yi ,yana tambayar sa

ina aka kwantar da shi,"nan ya sanar mai ,yace" ikon Allah

Asibitin da zahra ke ciki kenan,sallama sukai ya koma,shigar

sa Asibitin suka ci karo da Alhaji Tahir nan su ka gaisa ya

ke tambayar sa inda Alhaji yake ,take ya sanar mai ai Amaryar

sa ma ta haihu twince wani murna Alhaji Tahir yaji ta shige

shi Hameed ma ya murmushi.

Ak'alla yau kwanan Zahra 3 a Asibitin Alhaji kuma 2 yau dai

ya farfad'o amma baya iya magana Malam nai ya zo yana mai ya

Jiki duk jibga -jibagan sun cika d'aki sunki fita sai da suka

fita san nan ya kalli Alhaji yace" ka godewa Allah Fadima ta

sauka an samu 'yan biyu maza,Murmushi yai tayi,sai ga hawaye

Hannunsa ya d'aga sama ya na Addua ,nan Alhaji ya ce" ai suna

Asibitin nan" ta ke Malam ya futa,yai wa norse magana yana

son akai wa Mara lafiya ya ga twince da sauri ta debo su

cikin ikon Allah ba kowa d'akin,Alhaji har da Hawaye sai

kallon su yake yana murmushi Azuciyar sa yana godewa

Allah.

Alhaji Tahir ma ya shigo,ya gansu sun bashi sha 'awa nan yai

musu hud'uba da hassan nd hussain,ga su Kyawawa.

An sallami zahra yau suka biya d'akin Alhaji dakyar ta shiga

tana zubda hawaye ta kasa had'a ido dashi hannu ya d'aga ya

na nuna Alamar tazo ,su malam futa sukai,zuwa tai ta tsugunna

tana neman Afuwan sa, cikin nuna Alamar Nadama da hannu ya

nuna bakomi,Magana ta ji yayi yana cewa" zahra kiyi hakuri ba

laifin ki bane don duk naji gaskiya duk sharri da Makircin

mata na ne" ,Amma Nagode wa Allah daya bani Twince ki rik'en

su Amana wan nan takardun suna nan zan sa kid'auko ki aje

gunki" ,Ita kam tausayin sa take Ji dakyar ta tashi Goggo ta

shigo tana mai sannu ,ta Jata suka fita.

Zahra sunje hanyar futa taji An bangaje ta ta juya ganin

Nadiya tai take ta girgiza kai,Goggo ce tace" ke baki da

hankali ba kiga mara lafiya bace? zaki bangaje ta," taunar

chewgum take ,harda su kwai,tace "ke tsohuwa bana son shish

-shigi,zahra ta juya tace" Goggo kiyi hakuri mu tafi inde wan

nan ce zatai abunda yafi hakan 'yar rikon kishiyata ne hajiya

uwani",futa sukai suka tafi gida.

Urs Queen meemi [7:10pm, 31/08/2016] Queen meemiluv: ,

KISHIYOYINA NA QUEEN MEEMI

51

,Zainab kam fita tai can waje ta d'au boki tin..... Maigadi wanda yake cike da ruwan kumfa da alama wanki yake ,da gudu tai ciki ,d'akin da taga d'aya ta futo ne ta shiga ta kwara duk d'akin ya b'aci .....Magajiya.ta cakumo ta d tace"d'akin nawa zaki zuba wa ......Ruwan wanki ?

nan sukai ta fad'a duk da hajiyoyin sunfi k'arfin su amma kuma suda yarin ta... AJikin su sai da su kai kaca- kaca da falon..... Alokacin Zahra ta futo ganin hakan yasa ta fara kuka don ita abun ya fara isar ta bama tasan da zuwan su Anty Mariya ba,wayar Alhaji ta kiraa bugu d'aya ya d'auka ta gaya mai abun da ke faru wa ,ko Awa d'aya baiba ya shigo gidan........

A fusace! Ya shugo kirjin sa har ciwo yake,dama yana cike dasu,su... Mariya na ganin sa suka hau kuka,tambayar su yai ba 'asi ?nan suka ce" Munzo duba Jikin,zahra ne shine matan ka suka dake mu,"k'irjin sa ne ya ji yana ne man fashewa ,dafewa yai ya zauna ,da sauri suka zo .....Alhaji ?ya daka tar dasu ,tare da nuna musu k'ofa kowace ta bar mai gida karya bud'e ido ya gan su hakan yasa ...Jikinsu yai sanyi suka zari. Maya fai kowacce tai wa je su.

Mariya kuwa bayan sun duba zahra suka tafi ,tana zaune sae kuka ta ke ita kam auren nan Ya isheta ta rasa yanda zatai,wata zuciayar tace" mata kidage da addua mahakurci mawadaci

Malam umar wato baban zahra yaje inda Alhaji yake bussness na sa ,ganin sa yai kwance yana tunani bai ma san yazo ba ,sai daya bubbu ga san nan ya tashi... Aa malam ne ? zaun a wa yai yace"ashe zahra bata ji dad'i ba naso zuwa gidan to saena ga rashin dacewar saboda ga mata manya.

Alhaji yace ay daka zo kuwa kai da gidan surukin ka dariya suka sa...Alhajiya danja tsaki tare da dafe kai malam yace" ya de ?nan yace duk wata masifa wallahi mata na ke sani ,nan ya warware mai komai tun auren sa da zahra da kuma zubda mai da ciki da sukai har fad'an da akai yau.

KISHIYOYINA NA

QIEEN MEEMI

52

Cikin tashin hankali yace" assha !abu beyiba ,beji da d'in abunda su Mariya sukai ba, nan Malam mahaifin zahra keta bashi baki yadawo da matan sa bekama ta da girman su ace hakan tafaru ba, ....

Alhaji yace "da sun tsare mutuncin su da hakan bata faru ba .Zahra yarinya ce mai sauk'in kai su ba su gane ba ,malam kuwa.. Azuciyar sa tausayin Zahra yake ji ya san bai ma ta dede ba ya san tana hkr ,amma bayan da xai da k'addara,haka yata shi bayan sun sallama da...Alhaji.

Ya ta fi gida ransa ab'ace yana xuwa ko sallama goggo na d'aurin lemu ta kalle shi .Aa Malam! yan zu ka dawo? yace" barni kede ashe abunda yaran nan suka je sukai kenan"? ,suwa fa ?in ji... Goggo,nan ya zayya ne mata ,tafi ta au yi lalle ma! amma basu kyauta ba" ,ya kalle ta ina. Aminu yake ne ?suna cikin magana sai ga......Mujaheed

Kallon sa. Malam yai ,yace "kai? kira mun su .Mariya awaya ,kace" ina neman su tun da yanzu la 'asar tayi ,kace" masu.

Gobe da safe kowacce tazo ina nai manta "..Mujaheed yace to "baba bari na sayo kati",nan suka cigaba da tattauna wa akan zuban cikin zahra wanda ...Goggo tace gaskiya na raina wayon matan nan ace kunzau na kishi da 'yar cikin ku wlh sun kusa jika da ita haba da shirme in banda ma abun na ALLAH ne ina Zahra ina auren Alhaji,.

Ni wallahi... Alhajin keban tausayi .....Ma

No comments:

Post a Comment